Yanzu yanzunan Iran ta qaddamar da sabbin hare hare wa izraila

 Getty Images

Rundunar sojin Isra'la ta ce sabbin hare-haren Iran sun nufi cikin Isra'ila.

Cikin wani saƙo da rundunar ta wallafa a shafinta na Telegram, ta ce tana ƙoƙarin kakkaɓo hare-haren yayin da aka aike da saƙon gargaɗi ta waya ga mazauna yankunan da hare-haren suka dosa.


Kafar yaɗa labaran IRIB, mallakin gwamnatin Iran ta ce an fara ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami na Iran.

A wani labarin na daban ma'aikatar tsaron UAE ta ce ta kakkaɓo makamai masu linzami huɗu da jirage marasa matuƙa 25 da Iran ta harba ƙasar a ranar Lahadi.

Cikin wani saƙo da ma'aikatar ta wallafa a shafinta na X, ta ce tun bayan fara yaƙin Iran ta kakkaɓo makaman linzami fiye da 350 da jirage masara 

Comments

Popular Posts